
About
Shirin Duniyar Wasanni tare da Khamis Saleh a wannan makon ya mayar da hankali kan yadda Najeriya ta gaza samun gurbin alƙalin wasanni a gasar AFCON karo na biyu a jere.
A ƙarshen watan da ya gabata ne hukumar ƙwallon ƙafar Afrika CAF ta fitar da jadawalin alƙalan wasanni da za su bayar da gudunmawa a gasar cin kofin ƙasashen Afrika ta AFCON da zata gudana a Morocco cikin watan gobe, amma ba tare da alƙalin wasa ko guda ɗaya daga Najeriya ba.
Ko a makamanciyar gasar da ta gabata a Ivory Coast cikin shekarar 2024 babu wakilcin ko da alƙalin wasa guda daga Najeriyar, lamarin da ke matsayin babban koma baya ga wannan ƙasa ta tayi shura a fagen ƙwallo.
Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin...