Taƙaitaccen tarihi kan yadda aka faro gasar AFCON a shekarar 1957
15 December 2025

Taƙaitaccen tarihi kan yadda aka faro gasar AFCON a shekarar 1957

Wasanni

About

Shirin Duniyar Wasanni a wannan lokaci tare da Khamis Saleh ya yi duba ne kan tarihin gasar lashe kofin Afrika AFCON da hukumar CAF ke shiryawa.

An faro buga gasar lashe kofin nahiyar Afirka, wacce ke zaman gasar kwallon ƙafa mafi girma da daraja a nahiyar a shekarar 1957, da hukumar kula da kwallon ƙafar Afrika CAF ce ta jagoranci.

An fara gudanar da gasar ne a watan Fabrairun shekarar 1957 a birnin Khartoum na ƙasar Sudan da ƙasashe 3, kafin a shekarar 2019 aka faɗaɗata zuwa tawogogun ƙasashe 24, kuma Masar ce ta fara lasheta bayan lallasa Sudan da ta karbi baƙunci a wasan karshe, inda ta lashe kofin da aka sanya masa sunan Abdel Aziz Abdallah Salem, ɗan ƙasar Masar da ya fara shugabantar hukumar CAF.

Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.