
About
Send us a text
Gwamnatin Tarayya ta gayyaci Kungiyar Manyan Ma’aikatan Man Fetur da Iskar Gas ta Najeriya (PENGASSAN) da Matatar Dangote don a sasanta a yau.
Hakan ya biyo bayan umarnin da ’yan kwadagon suka bai wa mambobinsu ne na shiga yajin aiki bayan da Matatar Dangote ta salami ma’aikata fiye da 800.
Sai dai wasu masana suna ganin tun farko bai kamata lamarin ya kai ga haka ba da an bi wasu hanyoyi.
Wadannan hanyoyi shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai binciko.