
About
Send us a text
Harin da wasu ‘yan ta’adda suka kai kasuwar Daji da ke karamar hukumar Borgu a Jihar Neja ya sake jawo hankalin al’umma kan matsalar rashin tsaro da ke kara ta’azzara a yankunan karkara na Arewa ta Tsakiya. Kasuwar Daji, wadda ke zama cibiyar hada-hadar kasuwanci ga manoma, ‘yan kasuwa da mazauna kauyuka makwabta, ta kasance wuri na zaman lafiya kafin wannan mummunan lamari da ya girgiza mazauna yankin.
Batutuwa da dama daga kafafen yada labarai da dama sun bayyana mabanbantan ra’ayoyi kan batun.
Ko menene hakikanin abun da ya faru a wannan hari da ‘yan bindiga suka kai a kasuwar Daji?
Wannan shine batun da shirin Najeriya a yau na wannan lokaci zai yi duba akai.