Yadda hare-haren ta'addanci ke ci gaba da sanadin mutuwar mutane a Najeriya
12 July 2025

Yadda hare-haren ta'addanci ke ci gaba da sanadin mutuwar mutane a Najeriya

Mu Zagaya Duniya

About

Hukumar kare hakkin ɗan Adam ta Najeriya ta ce  adadin mutanen da ‘yan ta’adda suka kashe a cikin watanni shidan farko na wannan shekara, ya zarce adadin da aka lissafa a shekarar bara.

Ƙungiyar direbobin motocin dakon kaya a Senegal ta koka kan matsalolin tsaro da suka fara shafar yankunan kan iyakar ƙasarsu da Mali, inda ta yi barazar dakatar zirga-zirga zuwa Malin muddin mahukunta suka gaza ɗaukar matakan da suka ɗace.

Kakakin majalisar dokokin Kenyan ya goyi bayan bai wa ‘yan sandan Umranin harbe duk mai zanga-zangar da aka samu yana satar dukiyar jama’a da lalata kayan gwammnati.

A Amurka kuwa Ambaliyar ce ta yi sanadin mutuwar aƙalla mutane 119

Danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Nura Ado Sulaiman.