Skip to content
Opens in a new window
Cigaban kasuwar hannayen jari na nufin rayuwa ta fara inganta ga talakan Najeriya?
12 August 2026

Cigaban kasuwar hannayen jari na nufin rayuwa ta fara inganta ga talakan Najeriya?

Kasuwanci

About

A ƙarshen watan Yulin wannan shekara ta 2026, mujalar Bloomberg da ke bibiyar harkokin tattalin arzikin ƙasashen duniya, ta bayyana kasuwar hannayen jarin Najeriya a matsayin ta ɗaya a duniya a fannin dala, wajen yi wa ta Koriya ta Kudu fintinƙau.

Masana tattalin arziki sun alakanta wannan gagarumin ci gaba da kasuwar ta samu da sauye-sauye masu tsauri da gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu ta yi a fannin tattalin arziki.