Malamai a Najeriya na fuskantar tarin matsaloli saboda rashin kyawun albashi
07 October 2025

Malamai a Najeriya na fuskantar tarin matsaloli saboda rashin kyawun albashi

Ilimi Hasken Rayuwa

About

Shirin Ilimi Hasken Rayuwa tare da Shamsiyya Haruna a wannan makon ya mayar da hankali kan gudunmawar malaman makaranta ga rayuwar jama'a dai dai lokacin da aka gudanar da bikin ranar Malamai a sassa daban-daban na duniya.

Majalisar Ɗinkin Duniya ce ta ware wannan rana da nufin girmama gudunmawar da malaman ke bayarwa, sai dai an gudanar da wannan rana ne a dai dai lokacin da malamai a Najeriya dama sauran ƙsashen Afrika ke ganin ƙololuwar matsin rayuw sakamakon matsalolin da suka dabaibaye su kama daga rashin kyawun yanayin aiki dama ƙarancin albashi.

Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakken shirin...