
Makomar ilimi dalilin rufe makarantu sabida matsalar tsaro a Najeriya
Ilimi Hasken Rayuwa
A wannan makon shirin ya karkata akala ne kan makomar ilimi a Najeriya, inda hukumomi suka fara rufe makarantu saboda matsalolin tsaro da ke neman dakushe makomar ilimin manyan gobe. Me yasa jihohi ke gaggawar rufe makarantu bayan sace ɗalibai a Kebbi da Niger a kwanan nan? Shin babu wasu hanyoyin kawo ƙarshen matsalar tsaro sai dai rufe makarantu?
Tambayar kenan da ‘yan Najeriya ke yiwa gwamnatin ƙasar, yayin da ake ganin tarin jami’an tsaro na yiwa masu rike da manyan makamai rakiya, abin da ke nuna yawan jami’an tsaron da ƙasar ke da shi idan aka haɗa ƴansanda da sojoji da jami’an tsaron Civil Defence da sauransu, to kuwa iyaye suka ce idan har aka yi la’akari da wannan za a iya samarwa ɗalibai tsaro.
Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Shamsiyya Haruna.........