Opens in a new window
Yadda makomar ilimin yaran karkara a Najeriya ke cikin rashin tabbas
08 July 2026

Yadda makomar ilimin yaran karkara a Najeriya ke cikin rashin tabbas

Ilimi Hasken Rayuwa

About

A wannan makon, shirin ya nufi yankunan karkara, inda inda gine-ginen makarantu ke ci gaba da kasancewa a matsayin kango, kasancewar babu dalibai.

A wasu wuraren kuma, azuzuwan sun zama fanko, yayin da matasa da yara suka ƙaurace wa shiga, ‘yan mata na fita birni yin tallace-tallace, su kuma samari na dambatawa da aikin ƙwadagon fasa duwatsu da ɗiban yashi.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da sabon rahoton hukumar UNICEF ya nuna cewa, jihohin Kano, Katsina, da Jigawa ne ke kan gaba a faɗin Najeriya wajen yawan yaran da ba sa zuwa makaranta, inda a faɗin kasar kuwa, akwai yara sama da miliyan goma sha takwas da dubu ɗari uku da makoma ta iliminsu ke cikin haɗari.

Sau da yawa, wannan zargi na komawa ga gwamnati, sai dai abin tambayar shine, shin ko laifin na iyaye ne da al'umma, ko kuwa suma hukumomi akwai nasu kason?

Mun ziyarci garin Meshumi da ke karamar hukumar Ungoggo a jihar Kano, inda shirin ya tarar makarantar firamare na nan a gine, amma dakin karatu ya zama kufai.

Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin, tare da Shamsiyya Haruna