Opens in a new window
Taron ƙaddamar da littafin tarihi na wani fitaccen matashi a Kanon Najeriya
30 June 2026

Taron ƙaddamar da littafin tarihi na wani fitaccen matashi a Kanon Najeriya

Ilimi Hasken Rayuwa

About

Shirin na wannan mako ya mayar da hankali ne kan taron ƙaddamar da sabon littafin tarihin nan mai suna 'Mu San Magabata', wanda fitaccen matashin marubuci Kabiru Ahmad Kwalli ya rubuta da aka gudanar a jihar Kanon Najeriya.

Taron ya haɗa masana, sarakuna, da ɗandazon al'umma domin duba yadda za a ceto tarihin ƙasar Hausa da ke shirin bacewa.

Wannan littafi, kamar yadda masana da dama suka bayyana, ya zo ne a daidai lokacin da matasan yanzu ke ƙara nisanta da asalin tarihinsu.

To ko me ya sa mawallafin, Kabiru Ahmad Kwalli,  ya ɗauki tsawon lokaci yana wannan bincike? Ga abinda ya shaida mana lokacin da muke zantawa da shi.