Opens in a new window
Makomar ilimin yara a Kano na cikin halin rashin tabbas
14 July 2026

Makomar ilimin yara a Kano na cikin halin rashin tabbas

Ilimi Hasken Rayuwa

About

Shirin na wannan makon cigaba ne kan wanda muka gabatar a makon jiya, wanda ya gano yadda yara a wasu yankunan jihar Kano basa zuwa makaranta saboda yawon tallace-tallace domin tara kudin kayan ɗaki. Yayin da su kuma mazan suke diban yashi da fasa Dutse, da sunan wai su taso suna da sana'ar dogaro da kai.

Yankunan da wannan lamari yafi kamari sun hada da Challawa, Kafin Maiyaki, Madobi, Gora, da Kanwa. Idan ba a manta ba, a makon da ya gabata mun kawo rahoton yadda wasu makarantu suka koma dandalin shaye-shaye a garin Meshumi dake karamar hukumar Ungogo.