Opens in a new window
Hanyoyin Dawo Da Martabar Karatun Tsangaya A Najeriya
08 July 2026

Hanyoyin Dawo Da Martabar Karatun Tsangaya A Najeriya

Daga Laraba

About

An daɗe ana muhawara, musamman a Arewacin Najeriya, a kan buƙatar yin garambawul ga tsarin makarantun tsangaya.

A baya dai waɗannan makarantu kan samar da mahaddata alqur’ani waɗanda kuma sukan dogara da kai
Sai dai a wannan zamani, yaran da suke karatu a ƙarƙashin tsarin sun zama mabarata. 
Gwamnatoci da dama dai sun yi kokarin yin garambawul ga yadda ake gudanar da tsarin, amma ga alama haƙa ta kasa cimma ruwa.

Shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi Nazari ne kan hanyoyin da za a bi don magance matsalolin da suka dabaibaye harkar.