
About
Matsalar tsaro ta hare-haren da ‘yan ta’adda kan kai wa makarantu ko ɗalibai a sassan Najeriya, na ci gaba da ci wa al’ummar ƙasar tuwo a ƙwarya, la’akari da cewar ko a baya bayan nan, ‘yan bindiga sun kai hari tare da sace wasu ɗaliban wata Sakandare a ƙaramar hukumar Dekina da ke jihar Kogi.
Wannan ya zo ne bayan hare-haren da a makwannin baya makarantun suka fuskanta a jihohin Oyo da kuma Borno.
Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna da shugaban ƙungiyar Malaman Makarantu ta Najeriya, Comrade Audu Titus Amba.
Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.