Nasiru Garba Ɗantiye kan ƙorafin shugaban majalisar wakilan Najeriya game da yawan ciwo bashi
09 September 2025

Nasiru Garba Ɗantiye kan ƙorafin shugaban majalisar wakilan Najeriya game da yawan ciwo bashi

Bakonmu a Yau

About

Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya, Abbas Tajudeen, ya koka akan yadda bashi ya ke cigaba da yi wa ƙasar katutu, lamarin da ya ce yana barazana ga bunƙasar tattalin arziƙinta.

Tajuddeen, wanda ya bayyana haka jiya Litinin a Abuja, ya ce bashin da ke kan Najeriya a yanzu ya kai wani matsayi mai ban tsoro, inda ya ke kira da a sake fasalin yadda ake karɓar rance a ƙasar.

Akan haka ne Michael Kuduson ya tattauna da wani tsohon ɗan majalisar dokoki a ƙasar, Nasiru Garba Ɗantiye, ga kuma yadda tattaunawarsu ta gudana.