
01 April 2026
Mammane Wada kan shirin Nijar na kafa ƙungiyoyin samar da tsaro da basu makamai
Bakonmu a Yau
About
A Jamhuriyar Nijar, ra’ayoyi sun banbanta a kan shawarar da gwamnatin ƙasar ta yanke na kafa ƙungiyoyi waɗanda za ta bai wa horo tare da riƙe makamai don kare garuruwa daga hare-haren Ƴanbindiga.
A cewar gwamnati, jami’an ƙungiyoyin kare kan, za su kasance sojoji, da ƴansanda da sauran jami’an tsaron da suka yi ritaya, waɗanda za a riƙa biyansu kuɗin alawus.
Kan wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da Mammane Wada na ƙungiyar Transparency International da ke bibiyar lamurra a ƙasar ta Nijar.
Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu............