Gobe za a gudanar da zaɓen gwamna a jihar Ekiti ta kudancin Najeriya
19 June 2026

Gobe za a gudanar da zaɓen gwamna a jihar Ekiti ta kudancin Najeriya

Bakonmu a Yau

About

Gobe ne hukumar zaɓe a Najeriya ke gudanar da zaɓen gwamnan Ekiti da ke yankin kudanci, inda ƴan takara 13 za su fafata.

Ana kallon wannan zaɓen a matsayin zakaran gwajin dafi ga sabon shugaban hukumar zaɓen Farfesa Joash Amiputan.

Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da mai magana da yawun hukumar Hajiya Zainab Abubakar.

Latsa alamar sauti don sauraren yadda zantawarsu ta gudana...