
30 October 2025
Fatima Nzi Hassan kan ta'azzarar sauyin yanayi, yayin da ake gab da fara taron COP30
Bakonmu a Yau
About
Yayin da ake shirin fara taron sauyin yanayi na duniya da ake kira COP30 a Brazil, a ranar 10 ga watan gobe, ƙungiyar OXFAM ta fitar da sanarwa inda take sake bayyana damuwa a kan rashin ɗaukar kwararan matakai wajen aiwatar da yarjejeniyar da aka ƙulla shekaru 10 da suka gabata a birnin Paris.
Game da wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da darakatar ƙungiyar ta OXFAM a Nahiyar Afrika Malama Fatima Nzi Hassan.
Danna alamar saurare domin jin cikakkiyar tattaunawar.