
About
A Najeriya, Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta ƙaddamar da bincike akan zargin fitar bayan sirri daga rumbun ajiyar bayananta na masu zaɓe, wanda ya jamnyo cece-kuce a ƴan kwanakin nan.
Wannan ya biyo bayan wallafa bayan wani ɗan takara ne da ake zargin wani ma’aikacin INEC ya yi a dandalin sada zumunta a yayin zaɓwen fidda gwani na wata jam’iyyar siyasa a babban birnin tarayyar Najeriya Abuja.
Akan haka Michael Kuduson ya tattauna da Dakta Umar Yakubu, shugaban wata ƙungiyar farar hula a Abuja babban birnin Najeriya.