Opens in a new window
Dakta Sani Gambo kan taron ƙasashen ƙungiyar AES da Rasha
08 July 2026

Dakta Sani Gambo kan taron ƙasashen ƙungiyar AES da Rasha

Bakonmu a Yau

About

A wannan Laraba ake fara taron tuntuɓa tsakanin ƙasashen ƙungiyar AES wato Mali, Nijar da Burkina Faso da kuma  ƙasar Rasha a gefe guda a Yamai fadar gwamnatin  Nijar, inda ake sa ran za su tattauna batutuwan da suka shafi tsaro, tattalin arziki da kuma makamashi.

Wannan ne karo na biyu da ake gudanar taron bayan makamancinsa da aka yi a birnin Moscow na Rasha a watan Afrilun 2025, kuma ya na zuwa a daidai lokacin da mayaƙa masu ikirarin jihadi suka zafafa kai hare-hare a waɗannan ƙasashen na Sahel.

A kan wannan Oumarou Sani ya tattauna da Dakta Sani Gambo malami a jami’ar Andre Salifou da ke Zinder a Jamhuriyar Nijar, game da ci gaban da hakan zai kawo ga ƙasashen biyu.

Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.