Skip to content
Opens in a new window
Jamhuriyar Nijar ta gudanar da bikin ranar Hausa ta bana a ƙasar
15 September 2026

Jamhuriyar Nijar ta gudanar da bikin ranar Hausa ta bana a ƙasar

Al'adun Gargajiya

About

Shirin Al’adumu na gado a wannan makon ya sake waiwayar baukukuwan ranar Hausa ne ta Duniya, ranar da babban taronta ke gudana a dukkanin ranakun 26 ga watan Agusta duk shekara, to amma kasancewar bikin ya samu karɓuwa a gwamman ƙasashe ya sa bayan babban taron ake gudanar da wasu ƙarin bukukuwan ranar hausar ta Duniya a ƙasashe daban daban, ciki har da Jamhuriyar Nijar, inda aka gudanar da bikin zagayowar ranar hausar ta Duniya a ranar 8 ga watan Satumban da muke.

Ku danna alamar sauraro domin jin cikakken shirin tare da Nura Ado Sulaiman.